Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta samu tikitin shiga gasar cin kofin kwallon kafar Najeriya ta Super takwas.
Kungiyar Sai Masu Gida ta doke Sokoto United da ci 1-0 a ranar Asabar a filin wasa na Kano Pillars.
Kano Pillars ce ke kan gaba a rukunin A3 na Arewaci Northern Conference da maki 18.
Tawagar Evan Ogenyi da ta koma NNL a kakar wasan da ta wuce, za ta kara da Katsina United, Heartland FC, One Rocket da wasu kungiyoyi hudu a gasar Super Eight.
Kungiyoyi hudu ne za su samu tikitin shiga gasar cin kofin Super takwas zuwa gasar Firimiyar Najeriya a kakar wasa mai zuwa.
Za a buga wasan neman gurbin shiga gasar ta Najeriya a filin wasa na Stephen Keshi, Asaba.