Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta samu nasarar farko a waje, tun bayan fara gasar cin kofin kwararru ta kasa NPFL ta bana.
Kano Pillars ta samu nasara ne a kan kungiyar kwallon kafa ta Heartland da ci 1-0, a mintuna na 90.
Dan wasan Kano Pillars, Mark Daniel ne ya zura kwallo bayan da dan wasa David Ebuka ya tallafa masa wanda Kano Pillars ta samu nasara a waje a cikin gasar.