Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta koma filin wasa na Muhammad Dikkon jihar Katsina da buga wasannin ta na gasar cin kofin kwararru ta kasa wato NFPL.
NIGERIA TRACKER ta rawaito cewa, kungiyar Kwallon Kafa ta fada cikin rikici, tun bayan da aka mayar da filin wasa na Sani Abacha wurin keɓe masu killace cutar korona.
Tun daga wannan lokacin ne kungiyar kwallon kafa ta jihar Kano ke buga wasanta a Kaduna, kuma ta na fuskantar babban kalubale ko da a karawarsu ta karshe da suka yi rashin nasara a hannun Rivers United .
Da aka tuntubi jami’in yada labarai na kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars Rilwanu Idris Malikawa Garu ya tabbatar da komawar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars zuwa filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina inda za su buga wasa.