Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, ta bayyana mai tsaron gida Emeka Onyia ba ya nan ba tare da izini ba (AWOL).
Kano Pillars ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin.
Sai Masu Gida ya bayyana cewa an bata wanda ya ajiye harbin tun a watan Maris, 2025.
Kano Pillars ta jaddada cewa kokarin da mahukuntan kulob din da ma’aikatan kulab din suka yi na tuntubar shi ta hanyoyi daban-daban ya ci tura.
Wani bangare na sanarwar ya ce, “Onyia ya gaza zuwa horo kuma ya kasance ba ya nan gaba daya a sansanin kulob din ba tare da wata sanarwa ko hujja ba.”
“Wannan hali ya sabawa ka’idar aiki da kuma tsarin ladabtarwa na kungiyar, Kano Pillars FC tana daukar wannan lamari da matukar muhimmanci kuma za a dauki matakan da suka dace daidai da ka’idojin kulob din da kuma dokokin gasar Premier ta Najeriya.”