Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Hamisu Ibrahim Chidari ya jijinawa kungiyar bayar da agaji ta Boys Scout ta Jihar Kano bisa kokarinta na inganta tsaro da lafiyar alumma.
Kakakin Majalisar ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar a Majalisar Dokokin, ya na mai bayyana Kungiyar ta Boys Scout da cewar dadaddiyar kungiya ce da ta yi fice wajen bayar da gudunmawa a harkokin cigaba a birane da karkara.
Ya kuma ja hankalisu da su rike wannan kambun na su ta hanyar kara jajircewa a kan ayyukansu.
Cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran majalisar, Uba Abdullahi ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, sanarwar ta ce Chidari ya sha alwashin tallafawa Kungiyar akan wadansu ayyuka da ta bijiro da su, domin bunkasa harkokin Kungiyar.
A jawabinsa, Shugaban Kungiyar a Jihar nan, Alhaji Baffa Muhammad ya ce”Mun kawo ziyara Majalisar Dokokin ne, domin inganta zumunci tare da yabawa Kakakin Majalisar bisa yadda Majalisar ke aiki tukuru, domin inganta rayuwar alummar Jihar nan”.
Haka kuma ya godewa Kakakin Majalisar bisa kokarinsa na daukar dawainiyar wasu daga cikin ayyukansu.