fidelitybank

Kano: Na dauki wasu nauyin ayyukan kungiyar Boys Scout – Hamisu Chidari

Date:

Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Hamisu Ibrahim Chidari ya jijinawa kungiyar bayar da agaji ta Boys Scout ta Jihar Kano bisa kokarinta na inganta tsaro da lafiyar alumma.

Kakakin Majalisar ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar a Majalisar Dokokin, ya na mai bayyana Kungiyar ta Boys Scout da cewar dadaddiyar kungiya ce da ta yi fice wajen bayar da gudunmawa a harkokin cigaba a birane da karkara.

Ya kuma ja hankalisu da su rike wannan kambun na su ta hanyar kara jajircewa a kan ayyukansu.

Cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran majalisar, Uba Abdullahi ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, sanarwar ta ce Chidari ya sha alwashin tallafawa Kungiyar akan wadansu ayyuka da ta bijiro da su, domin bunkasa harkokin Kungiyar.

A jawabinsa, Shugaban Kungiyar a Jihar nan, Alhaji Baffa Muhammad ya ce”Mun kawo ziyara Majalisar Dokokin ne, domin inganta zumunci tare da yabawa Kakakin Majalisar bisa yadda Majalisar ke aiki tukuru, domin inganta rayuwar alummar Jihar nan”.

Haka kuma ya godewa Kakakin Majalisar bisa kokarinsa na daukar dawainiyar wasu daga cikin ayyukansu.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp