fidelitybank

Kano: Na dauki wasu nauyin ayyukan kungiyar Boys Scout – Hamisu Chidari

Date:

Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Hamisu Ibrahim Chidari ya jijinawa kungiyar bayar da agaji ta Boys Scout ta Jihar Kano bisa kokarinta na inganta tsaro da lafiyar alumma.

Kakakin Majalisar ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin Kungiyar a Majalisar Dokokin, ya na mai bayyana Kungiyar ta Boys Scout da cewar dadaddiyar kungiya ce da ta yi fice wajen bayar da gudunmawa a harkokin cigaba a birane da karkara.

Ya kuma ja hankalisu da su rike wannan kambun na su ta hanyar kara jajircewa a kan ayyukansu.

Cikin wata sanarwa da daraktan yada labaran majalisar, Uba Abdullahi ya sanyawa hannu a ka kuma rabawa manema labarai, sanarwar ta ce Chidari ya sha alwashin tallafawa Kungiyar akan wadansu ayyuka da ta bijiro da su, domin bunkasa harkokin Kungiyar.

A jawabinsa, Shugaban Kungiyar a Jihar nan, Alhaji Baffa Muhammad ya ce”Mun kawo ziyara Majalisar Dokokin ne, domin inganta zumunci tare da yabawa Kakakin Majalisar bisa yadda Majalisar ke aiki tukuru, domin inganta rayuwar alummar Jihar nan”.

Haka kuma ya godewa Kakakin Majalisar bisa kokarinsa na daukar dawainiyar wasu daga cikin ayyukansu.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp