fidelitybank

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Date:

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, ta fitar kan alƙaluman makon farko na mutanen da suka nuna aniyar yin rajistar zaɓe ta intanet sun nuna cewa al’umma ba su fito sosai ba a yankin arewacin ƙasar domin yin rajistar.

Alƙaluman da hukumar ta Inec ta fitar a jiya Litinin sun nuna cewa jihar Osun ce ta fi yawan mutanen da suka nuna aniyar yin rajistar, inda take da yawan mutane 393,269, jihar Legas ke biye mata da mutum 222,205 sai kuma jihar Ogun mai yawan masu son yin rajista 132,823.

A arewacin Najeriya, Abuja, babban birnin tarayyar ƙasar ne ke da mafi yawan mutanen da suka nuna aniyar yin rajista, inda take da mutum 107,683, sai jihar Kaduna mai mutum 61,512 yayin da jihar Kogi ke biye mata da mutum 58,546.

Jihar Kano wadda ta fi kowace yawan al’umma a Najeriya na da yawan waɗanda suka nuna aniyar yin rajistar zaɓe 10,166 ne, Adamawa kuma na da 2,115 kacal.

Sai dai idan aka duba ƙasar baki ɗaya za a ga cewa yankin kudu maso gabashin ƙasar shi ne ya fi ƙarancin mutanen da suka nuna aniyar yin rajista a makon na farko.

Jihar Enugu na da mutum 484, Imo 481 sai kuma jihar Ebonyi mai mutum 261 kacal.

A ranar 18 ga watan Agusta ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta buɗe shafinta na intanet domin mutane su nuna aniyar yin rajistar katin zaɓe.

Alƙaluman na Inec sun nuna cewa ya zuwa ranar Lahadi 24 ga watan na Agusta an samu mutum miliyan 1,379,342 waɗanda suka nuna sha’awar yin rajistar ta shafin intanet.

Ya zuwa yanzu alƙaluman na Inec sun ce mata ne waɗanda ke gaba a yawan wadanda suka nuna aniyar yin rajista a fadin ƙasar, inda suke da kashi 52.04% yayin da maza ke da kashi 47.96%.

Daga nan sai hukumar ta sanar da cewa ta buɗe rumfunanta a fadin ƙasar domin bai wa mutane damar zuwa ƙafa-da-ƙafa domin yin rajista.

Aikin yin rajistar zaɓen na zuwa ne gabanin babban zaɓen shekara ta 2027, inda tuni jam’iyyu da kuma masu neman takara suka fara shiri.

Yanzu haka dai ƙasar ta Najeriya mai yawan mutum sama da miliyan 200 na da mutane miliyan 93,469,008 da suka yi rajistar zaɓe a faɗin ƙasar.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...

Kano na cikin jihohin da ba su yi katin zabe sosai ba – INEC

Bayanan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya...

Mun gano filin wasa na Sani Abacha ba shi da inganci – NPFL

Hukumar shirya gasar cin kofin kwararru ta kasa (NPFL),...

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya ya fadi

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinjoji da ya taso daga...

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...
X whatsapp