Gwamnatin jihar Kano ta sanar da ɗage ranar komawa hutun ɗaliban makarantun sakandire da na furamare a faɗin jihar.
Tun da farko dai an tsara cewa ɗaliban makarantun kwana a faɗin jihar za su koma makarantun a yau Lahadi 8 ga watan Satumba, yayin da ɗaliban makaratun je-ka-ka-dawo za su koma ranar Litinin 9 ga watan Satumbar.
To sai dai cikin wata sanarwa da darakta wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimin jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya fitar ranar Asabar, ya ambato kwamishinan ilimin jihar, Umar Haruna Doguwa, na cewa an ɗage ranar komawa makarantun, sakamakon wasu dalilai da ya ce za su ”taimaka wajen inganta harkar koyo da koyarwa a makarantun jihar”.
”Nan gaba kaɗan za a sanar da sabuwar ranar komawa makarantar”, in ji sanarwar.
Can ma a jihar Edo da ke kudu maso kudancin ƙasar gwamnatin jihar ta sanar da dakatar da komawa makarantun har sai abin da hali ya yi sakamakon ƙarin farashin man fetur.
Cikin sanarwar matakin da babban sakataren ma’aikatar ilimin jihar, Ojo Akin-Longe, ya fitar ranar Asabar, ya ce matakin ya zama wajibi sakamakon halin da iyaye ciki bayan ƙarin kuɗin man fetur da wasu ƙarin matsaloli.