Hukumar kididdiga ta kasa NBS ta saki jerin jihohin Najeriya da a ka fi kira da waya da kuma amfani da yanar gizo a rubu’in karshe na shekarar 2021.
NBS ta bayyana cewa, idan a ka kwatanta adadin masu kira a waya da amfani da shafin Internet a shekarar 2020, adadin na 2021 ya ragu.
A jawabin da NBS ta daura a shafinta na internet ta ce, a rubu’in karshe na 2021, jimillar mutum 195,463,898 suke kira a waya sabanin rubu’in karshe na 2020 da aka samu mutum 204,601,313.
Hakazalika mutum 141,971,560 sukayi amfani da yanar gizo.” “Jihar Legas ke kan gaba. biye da jihar Kano da Ogun, yayinda jihar Bayelsa da Ebonyi ne masu mafi karanci.
Ga jerin jihohi 10 da akafi kira a waya da amfani da yanar gizo: 1. Lagos: 18.9m 2. Kano: 9.6m 3. Ogun: 9.1m 4. Oyo: 8m 5. Abuja: 6.9m 6. Kaduna: 6.8m 7. Rivers: 5.7m 8. Delta: 5.3m 9. Edo: 5.2m 10. Niger: 4.9m.