fidelitybank

Kano ce koma baya a jihohi 18 a fannin mafi karancin aiwatar da aiki – CEDEHUR

Date:

Cibiyar kare dimokuradiyya da kare hakkin dan Adam ta CEDEHUR, ta ayyana jihar Kano ta fuskar sha’anin mulki a matsayin koma baya, kuma mafi karanci a aiwatar da aiki a kasar nan, tun bayan da sabuwar gwamnati ta hau mulki a watan Mayun 2023.

Cibiyar ta yi wannan ikirarin ne a ranar Talatar a Abuja, yayin da take gabatar da rahotonta na kashi uku kan yadda ake gudanar da sha’anin mulki a jihohi 18 tare da sabbin gwamnoni.

Cibiyar ta ce an gudanar da tantancewar ne bisa gaskiya da rikon amana da ingancin wadanda aka nada da kuma tasirin manufofin da suka shafi al’ummar jihohin 18.

Da yake jawabi a madadin Cibiyar, Amb. Adebayo Lion Ogorry ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa, Kano ta kasance a matsayin mafi kasa ta fuskar shugabanci na gari, yana mai zargin cewa gwamnati mai ci ta mayar da hankali ne kan tsarin siyasa mafi koma baya.

Ya kuma ce, Kano na daya daga cikin Jihohin da Gwamnansu ya samu matsala ta bangarori da dama.

Daga kididdigar da ake da ita, jihar ta tsunduma cikin harkokin siyasa da suka shafi harkokin mulki.

Daily Post ta rawaito cewa, gwamnan jihar yana da ra’ayin magance matsalolin zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

Sai dai Ogorry ya kara da cewa, nade-naden mukaman da aka yi a Kano, an yi ne bisa la’akari da gudunmawar da mutanen suka ba shi a siyasa ba wai domin saboda gogewa ko cancantar su ba.

 

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp