Da sanyin safiyar wannan ranar ta litinin ne aka wayi gari da labarin cewa Allah ya yiwa shahararren jarumin fim din Kannywood, Alhaji Kabiru Nakwango.
Labarin ya yi ta zagayawa musamman a kafafen sada zumunta, Inda mutane da dama suka nuna damuwarsu bisa Rashin Dan wasan da aka ce an yi.
Makusantan jarumin mun gano labarin Rasuwar ta Nakwango ba shi da tushe ballantana Makama. A cewar Kadaura24.
Abba El-Mustapha jarumi ne a masana’atar Kannywood a sahihin shafinsa na Facebook muga ya musanta labarin rasuwar Nakwangon kamar yadda ake cigaba da yadawa a kafafen sada zumunta.
“Yanzu mukayi waya da MALAM KABIRU NAKWANGO mu ka gaisa muka dan taba barkwancinmu da muka saba yi dashi. Daga karshe yace in gaishe masa da masoyansa na page dina. Shi yanzu haka ma ya tafi gonarsa domin gewaya”. Inji Abba El-Mustapha.
Dama dai lokaci zuwa lokaci akan kirkiri labarai na Karya musamman mutuwa a danganta ta ga jaruman fina-finan Kannywood.