Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya yi ikirarin cewa, gadar Neja ta biyu da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta aiwatar, ta isa yankin Kudu maso Gabas su zabi Bola Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Gwamna Uzodinma ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a cikin shirin gidan Talabijin na Channels.
Gwamnan ya kuma ce, galibin hanyoyin gwamnatin tarayya a shiyyar sun samu isasshiyar kulawa da hukumar kasafin kudi, inda ya kara da cewa matafiya ba sa shan wahala kamar yadda suke yi a da.
“Sanata Bola Tinubu ne dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, jam’iyyar da ke mulki. Daga 1970 lokacin da yakin basasa ya kare, Igbos sun nemi gadar Neja ta biyu, gwamnati bayan gwamnati ta zo da alkawuran da ba a cika ba.
Abun da ya faru a Kano ya nuna nasarar Tinubu ƙarara – Keyamo
“An yi wa Kirsimetin da ya gabata murna da murna, ‘yan kabilar Igbo sun fito daga wajen Kudu maso Gabas suna amfani da gadar Neja ta Biyu. Hakan ma ya isa duk ‘yan kabilar Igbo su zabi gadon Buhari ya ci gaba,” in ji Uzodinma.