Cibiyar bunƙasa ciniki da masana’antu da ma’adinai da ayyukan gona (KACCIMA) ta Jihar Kano, ta ce aƙalla kamfanoni 300 daga cikin da wajen Najeriya za su halarci baje-kolin kasuwar duniya ta bana wanda shi ne karo na 45 a jihar Kano.
Ana sa ran kasuwar za ta ci ne tsakanin 23 ga Nuwamba zuwa 7 ga Disamban 2024.
Shugaban KACCIMA, Alhaji Garba Imam ya bayyana haka, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, inda ya ƙara da cewa ana sa ran kamfanoni daga ƙasashen India da Nijar da sauransu za su zo su baje-kolin kayayyakinsu.
Imam ya ƙara da cewa cibiyar ta tanadi dukkan abubuwan da ake buƙata domin tabbatar da an ci kasuwar sumul, “sannan kuma mun mayar da shiga kasuwar kyauta domin ba mutane da dama damar zuwa.”
Shugaban na KACCIMA ya ce mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Kashim Shettima ne zai buɗe baje-kolin, sannan gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf zai zama babban mai masaukin baƙi, sannan ya ƙara da cewa akwai isasshen tsaro.