fidelitybank

Kamfanoni 300 sun karye a Najeriya saboda faduwar Naira – MAN

Date:

Ƙungiyar masu kamfanonin samar da kayayyaki a Najeriya, MAN, ta ce kamfanoni kusan dari uku ne suka durƙushe tun bayan da aka fara samun karyewar darajar kuɗinƙasar, Naira.

Karyewar darajar naira dai ta jefa tattalin arzikin Najeriya cikin wani hali, lamarin da masu masana’antun ke cewa suma basu tsira ba.

Alhaji Sani Hussaini mamba a majalisar zartarwa a ƙugiyar kamfanoni a Najeriya, ya ce faɗuwar darajar naira ta kai ga tashin sama da kashi ɗari na abubuwan da suke sarrarafawa.

Kuma ba za su iya ƙara farashin kayyakinsu ya kai wannan farashinba a kasuwa.

Haka zalika kayan abinci su ne suka fi tafiya a kasuwa, lamarin da ya sa idan ba su kamfani ke sarrafawa ba, kasuwarsa na ci baya.

Inda ya ce kashi 80 cikin ɗari na kayyakin da kamfanonin ke amfani da su shigo da su a keyi daga waje.

Lamarin da ya ce ya jefa wasu ƙarin kamfanoni kimanin 150 cikin tangal-tangal.

Daidaituwar farashin kuɗaɗen waje, musamman dalar Amurka, a cewarsa zai taimaka gaya wajen tafiyar da ayyukan kamfanoni da masana’antu a ƙasar.

Tun bayan bullo da garambawul ta fuskokin da suka haɗa da janye tallafin man fetur da daidaita kasuwar musayar kuɗaɗen wajen a bara ne, ƙasar ta shiga wani hali.

Yayin da al’ummarta ke ci gaba da kokawa kan tsadar rayuwa.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp