Kamfanin sada zumunta na Twitter ya ce, ya yi rijista a matsayin kamfani karkashin dokokin Najeriya, cikin watanni bayan da kamfanin ya amince da sharuddan da gwamnatin ta gindaya kafin ta kyale shi ya ci gaba da aiki a cikin kasar.
Najeriya ta dakatar da kamfanin a watan Yunin bara ne bayan da ya goge wani sako da Shugaba Muhammadu Buhari ya wallafa.
Twitter ya kare kansa, yana cewa sakon ya taka tsarin aikinsa, sai dai gwamnatin Najeriya ba ta gamsu da matakin ba.
Sai bayan wata bakwai Najeriya ta dage hanin wato a watan Janairun bana, shi ma sai da Tiwita ya amince da wsu sharudda, cki har da yin rajista a kasar kafin karshen watan Maris.
Wani wakilin kamfanin ya tabbatar wa BBC cewa kamfanin ya cika wadannan bukatun.