fidelitybank

Kamfanin mai na NNPCL ya ayyana dokar ta bace

Date:

Kamfanin man fetur na kasa NNPCL, ya ayyana dokar ta-ɓaci kan harkokin haƙowa da kuma fitar da ɗanyen mai daga ƙasar nan.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari, ya ce an ɗauki matakin ne da zimmar haɓaka yawan man da ake haƙowa, yana mai cewa bincike ya nuna Najeriya za ta iya haƙo fiye da ganga miliyan biyu duk rana.

Ya ce, an ayyana yaƙi ne a kan ƙalubalen da ake fuskanta a harkokin haƙo fetur.

Mele Kyari da yake magana a taron masu ruwa da tsaki a harkar mai ta kasa a yau Talata a Abuja, ya ce, sun shaida wa abokan hulɗar su, cewa akwai isashen kayan aikin hakan man.

Ya ƙara da cewa, yaƙin zai taimaka wa NNPCL da abokan hulɗarsa na kawo ƙarshen duka matsalolin, domin cigaba da haƙowa da sayar da man ba tare da tsaiko ba.

Da yake magana kan motoci amfani da iskar gas na CNG, Kyari ya ce tuni kamfanin ya gina tashoshin iskar gas na CNG, inda za su ƙaddamar da 12 daga ciki a Legas ranar Alhamis mai zuwa.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp