Babban kamfanin mai na Najeriya NNPCL na gudanar da jarrabawar ɗaukar sabbin ma’aikata.
Cikin wani saƙo da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X, ya ce kimanin mutum 45,689 ne suke gudanar da jarrabawar wadda aka yi da kwamfuta.
”A yau NNPCL ya fara gudanar da jarrabawar ɗaukar ma’aikata da ake gudanarwa ta hanyar kwamfuta a cibiyoyi da dama a faɗin ƙasar nan”, in ji sanarwar.
NNPCL ya bayyana tsarin ɗaukar ma’aikatan da cewa tsari ne da yake gudanarwa a bayyane domin bai wa kowa dama.
”Domin damawa a kowa wajen ɗaukar aiki, NNPCL ya yi tanadi na musamman domin tabbatar da masu lalurar buƙata ta musamman da ke cikin masu neman aikin, sun samu damar gudanar da jarrabawar ba tare da wata matsala ba”, kamar yadda kamfanin ya wallafa a shafinsa na X