fidelitybank

Kamfanin jiragen sama za su fara biyan diyya ga fasinjoji – Gwamnatin Tarayya

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce nan ba da dadewa ba, za ta tilasta wa kamfanonin jiragen sama su fara biyan diyya ga fasinjoji saboda jinkiri ko soke tashi jirgi, matuƙar ba wani al’amari ne daga Allah ya haddasa matsala ba.

Gidan talbijin na Channels ya ambato ministan sufurin jiragen saman Najeriya, Festus Keyamo na bayyana haka lokacin da yake ganawa da kamfanonin jiragen sama a Abuja ranar Litinin.

“Dangane da jinkiri ko soke tashin jirgin sama, ina so na tabbatarwa al’ummar Najeriya da ke korafi a kullum game da irin wannan matsalar, za mu fara aiwatar da tanade-tanaden dokar Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya’ wadanda ‘yan Najeriya ba su san da su ba,”

“Wannan tanadi shi ne kamfanonin jiragen sama za su biya diyya a kan jinkiri ko soke tashin jirgi, matuƙar ba wata matsala ce ta faru sanadin wani al’amari daga Allah ba.

“Amma idan wani al’amari ne daga Allah, babu wata diyya da za su biya.”

Sai dai Keyamo ya bukaci ma’aikatan kamfanonin jiragen sama su samar da hanyoyin sadarwa tabbatattu da ke bai wa fasinjoji damar samun bayanai a kan jinkiri ko sokewar tashin jiragen sama.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp