Mahukuntan kamfanin jiragen Arik Air Limited da Aero Contractors, sun ce za su fara gudanar da dukkan zirga-zirgar jiragensu a ranar Litinin 9 ga Mayu, 2022.
Kamfanonin jiragen sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar tare da mikawa manema labarai a ranar Lahadi a Legas.
Sanarwar hadin guiwar ta ce: “Dukkanin hukumomin biyu sun yi cikakken bayanin tare da amincewa da kokarin da Kamfanin Jiragen Sama na Najeriya (AON) ke yi na samar da yanayi na kauracewa zirga-zirgar jiragen, saboda tsadar farashin JET A1.
“Duk da haka, muna da tabbacin cewa, gwamnati na duba batutuwan da AON ta gabatar kuma za ta yanke shawarar da za ta fi dacewa ga masana’antu da kuma jama’a masu tafiya.”
Sanarwar ta kara da cewa “Fasinjojin da aka ba su izinin yin balaguro a kan kamfanonin Arik da Air Aero Contractors gobe da kuma bayan su, su wuce zuwa filayen saukar jiragen sama na tashi,” in ji sanarwar.