Kamfanin haƙar ɗanyen man fetur na Shell zai biya diyyar yuro miliyan 15 (dala miliyan 15.9) ga mazauna yankin Neja-Delta waɗanda malalar man fetur ta shafa.
Alƙawarin biyan diyyar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Juma’a tare da haɗin gwiwar reshen cibiyar Friends of the Earth a ƙasar Netherlands.
Matakin ya biyo bayan hukuncin kotun Netherlands inda ta kama reshen kamfanin na Shell a Najeriya da laifin malalar mai a shekarar da ta wuce kuma ta umarci Shell ya biya diyya.
Tun a shekarar 2008 manoma daga Neja-Delta tare da taimakon Friends of the Earth suka gurfanar da Shell a gaban kotun da ke The Hague sakamakon gurɓata musu muhalli da ya yi a tsawon shekarun da ya shafe yana haƙo albarkatun fetur a yankin.