fidelitybank

Kamata ya yi ‘yan Najeriya su gode mana a kan kokarin mu – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce, da ‘yan ƙasar sun san irin halin matsi da takwarorinsu na ƙasashen Afirka ke ciki da sun gode wa Allah.

A wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kan kafofin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar, ya ce shugaban ya fadi hakan ne ranar Asabar lokacin da ya kai wa Sarkin Katsina Dr Abdulmumini Kabir Usman ziyara a fadarsa.

Ya kara da cewa ”Muna kira ga mutane da su yawaita haƙuri, muna iya bakin ƙoƙarinmu. Babu abin da ya fi zaman lafiya, muna roƙon Allah ya ba mu damar ganin bayan masu ƙoƙarin wargaza mana zaman lafiyar ƙasarmu.”

Shugaban ya kuma ce, zai ci gaba da yin bakin ƙoƙarinsa wajen yalwata wa ‘yan kasar bayan jin ƙorafe-ƙorafe kan halin da ‘yan ƙasar ke ciki daga bakunan gwamnan jihar Aminu Bello Masari da kuma Sarkin Katsina.

”Da mutanenmu sun san irin halin matsin rayuwa da wasu ƙasashen Afirka ke ciki a halin yanzu, da sun gode wa Allah game da halin da suke ciki a ƙasar nan,” in ji Shugaban na Najeriya.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki...

‘Yan Bindigar Katsina ‘yan asalin jihar mu ne – Gwamna

Gwamnan Katsina Umaru Dikko Radda ya ce galibin 'yan...

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya...

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari...

Ganduje ya kama aiki a hukumar kula da filayen jirgin sama

Tsohon shugaban jam'iyyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya...

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...
X whatsapp