fidelitybank

Kamata ya yi Facebook ya dakatar da gwamnatin Najeriya – Lauyan Kanu

Date:

Lauyan kasar Amurka, Bruce Fein, wanda ya ke kare Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, ya bukaci Facebook da ya haramtawa gwamnatin Najeriya.

A cewarsa, ya kamata Facebook ya yi la’akari da sanya takunkumi ga gwamnatin Najeriya, bisa zargin kisan kiyashi da cin zarafin bil’adama da ake yi wa kungiyar IPOB da al’ummar yankin kudu maso gabas.

Daily Post ta rawaito cewa, roko na sa ya biyo bayan kiran da Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu ya yi, na neman Facebook ta haramtawa kungiyar IPOB amfani da kafafen sada zumunta.

Mohammed ya ce, Facebook bai taka rawar gani ba wajen hana kungiyar IPOB tada zaune tsaye ta hanyar amfani da dandalin.

Fein a cikin wata wasika da ya aike wa Mark Zuckerberg, wanda ya kafa Facebook ya ce, “Ina sane da yadda gwamnatin Najeriya ta yi kakkausar suka ga Facebook na haramta kungiyar IPOB da mambobinta daga dandalin sada zumunta bisa zargin tayar da rikici. Wannan yunƙurin dai na nuni ne kan matakin gwamnatin Najeriya na haramta kungiyar IPOB a matsayin kungiyar ta’addanci a watan Satumban 2017. Dukkan labarin ya kara bayyana.

“Tsarin dokar ya sabawa tsarin da ya dace. An hana IPOB sanarwar da kuma damar mayar da martani. Wannan haramcin shi ne rashin gaskiya ipse dixit na shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.

“Saboda haka, ina rokon a cikin girmamawa da Facebook ya tsawata wa gwamnatin Najeriya da ke karkashin mulkin Fulani saboda neman tauye hakkin ‘yan kungiyar ta IPOB.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp