Lauyan kasar Amurka, Bruce Fein, wanda ya ke kare Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, ya bukaci Facebook da ya haramtawa gwamnatin Najeriya.
A cewarsa, ya kamata Facebook ya yi la’akari da sanya takunkumi ga gwamnatin Najeriya, bisa zargin kisan kiyashi da cin zarafin bil’adama da ake yi wa kungiyar IPOB da al’ummar yankin kudu maso gabas.
Daily Post ta rawaito cewa, roko na sa ya biyo bayan kiran da Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu ya yi, na neman Facebook ta haramtawa kungiyar IPOB amfani da kafafen sada zumunta.
Mohammed ya ce, Facebook bai taka rawar gani ba wajen hana kungiyar IPOB tada zaune tsaye ta hanyar amfani da dandalin.
Fein a cikin wata wasika da ya aike wa Mark Zuckerberg, wanda ya kafa Facebook ya ce, “Ina sane da yadda gwamnatin Najeriya ta yi kakkausar suka ga Facebook na haramta kungiyar IPOB da mambobinta daga dandalin sada zumunta bisa zargin tayar da rikici. Wannan yunƙurin dai na nuni ne kan matakin gwamnatin Najeriya na haramta kungiyar IPOB a matsayin kungiyar ta’addanci a watan Satumban 2017. Dukkan labarin ya kara bayyana.
“Tsarin dokar ya sabawa tsarin da ya dace. An hana IPOB sanarwar da kuma damar mayar da martani. Wannan haramcin shi ne rashin gaskiya ipse dixit na shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.
“Saboda haka, ina rokon a cikin girmamawa da Facebook ya tsawata wa gwamnatin Najeriya da ke karkashin mulkin Fulani saboda neman tauye hakkin ‘yan kungiyar ta IPOB.