fidelitybank

Kamata ya yi a rinka jefe masu neman jinsi – Shugaban Burundi

Date:

Shugaban Burundi, Evariste Ndayishimiye, ya ce, ya kamata a jefe masu neman jinsi abin da a cewarsa yin hakan ba zai zama laifi ba.

A wani taron ƴan jarida ranar Juma’a, yayin da yake mayar da martani game da tambayar da wani ɗan jarida ya yi masa ya ce Burundi ba ta buƙatar agajin manyan ƙasashe masu ƙarfin iko su “su ajiye taimakonsu” idan har yin hakan na tare da buƙatar neman a bai wa masu neman jinsi dama.

A jawabin nasa, shugaban ya yi misali da Injila inda ya ce Ubangiji ya yi hani da neman jinsi inda ya ce neman jinsi sam ba batu bane a Burundi.

“A wurina, ina ganin idan muka ga masu irin wannan aƙida a Burundi, a kai su filin wasa a jefe su, kuma yin hakan ba zai zama laifi ba,” kamar yadda shugaban ƙasar ta Burundi ya ce.

Mr Ndayishimiye ya ce neman jinsi kamar yin zaɓi na tsakanin shaiɗan da Ubangiji”.

“Idan kana son zaɓar Shaiɗan, toh ka je ka yi rayuwa a irin ƙasashen kuma ina tunanin masu fafutukar zuwa can suna son rungumar ɗabi’un, ya kamata su tsaya a can kada su kuskura su kawo mana su.” in ji shugaban.

Burundi dai ta haramta neman jinsi kuma laifi ne da ke iya janyo hukuncin kusan shekara biyu a gidan yari.

A watan Agusta, mutum bakwai aka yankewa hukuncin shekara tsakanin daya zuwa biyu a gidan yari bayan da kotu a Gitega ta same su da laifin neman jinsi tuhumar da suka musanta.

www.punch news.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp