fidelitybank

Kamaru ta gargaɗi masu yaɗa an yi juyin mulki

Date:

Ministan sadarwa na ƙasar Kamaru, Rene Emmanuel Sadi, ya yi gargadi game da raɗe-raɗin da ake yi cewa kasar na iya fuskantar juyin mulki, a daidai lokacin da ake fama da matsalar a ƙasashen Afirka waɗanda Faransa ta yi wa mulkin mallaka.

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnatin kasar ya fitar, ya bayyana Kamaru a matsayin ƙasa ta masu bin doka tare da barazanar kamawa da hukunta masu hasashen juyin mulki a ƙasar.

“Saboda haka gwamnati ta buƙaci mutane da su yi taka-tsan-tsan don kada su yaɗa jita-jitar juyin mulki da kuma hasashen makomar Kamaru, lamarin da zai iya tayar da zaune tsaye a ƙasar” in ji shi.

Tun bayan da sojoji a Gabon suka kwace mulki daga hannun Ali Bongo a ranar 30 ga watan Agusta, masu sharhi kan shafukan sada zumunta ke ci gaba da ƙara nuna yiwuwar juyin mulki a makwabciyarta, kasar Kamaru.

Shugaba Paul Biya mai shekaru 90 wanda ya tsallake rijiya da baya a yunƙurin juyin mulki a ƙasar a shekarar 1984 ya shafe shekaru 41 yana mulkin Kamaru.

Magoya bayansa na neman ya sake tsayawa takara a zaben 2025.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp