fidelitybank

Kamaru ta gargaɗi masu yaɗa an yi juyin mulki

Date:

Ministan sadarwa na ƙasar Kamaru, Rene Emmanuel Sadi, ya yi gargadi game da raɗe-raɗin da ake yi cewa kasar na iya fuskantar juyin mulki, a daidai lokacin da ake fama da matsalar a ƙasashen Afirka waɗanda Faransa ta yi wa mulkin mallaka.

A cikin wata sanarwa da kakakin gwamnatin kasar ya fitar, ya bayyana Kamaru a matsayin ƙasa ta masu bin doka tare da barazanar kamawa da hukunta masu hasashen juyin mulki a ƙasar.

“Saboda haka gwamnati ta buƙaci mutane da su yi taka-tsan-tsan don kada su yaɗa jita-jitar juyin mulki da kuma hasashen makomar Kamaru, lamarin da zai iya tayar da zaune tsaye a ƙasar” in ji shi.

Tun bayan da sojoji a Gabon suka kwace mulki daga hannun Ali Bongo a ranar 30 ga watan Agusta, masu sharhi kan shafukan sada zumunta ke ci gaba da ƙara nuna yiwuwar juyin mulki a makwabciyarta, kasar Kamaru.

Shugaba Paul Biya mai shekaru 90 wanda ya tsallake rijiya da baya a yunƙurin juyin mulki a ƙasar a shekarar 1984 ya shafe shekaru 41 yana mulkin Kamaru.

Magoya bayansa na neman ya sake tsayawa takara a zaben 2025.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp