fidelitybank

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Date:

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi na da alaƙa shigarsa cikin haɗakar jam’iyyun hamayya.

Atiku ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook, inda ya zargi gwamnatin Tinubu da yunƙurin cin zarafi da tsoratarwa da nufin murƙushe jam’iyyun hamayya a ƙasar.

“Abun da muke gani a yanzu shi ne yadda gwamnatin Tinubu ke amfani da yaƙi da cin hanci a matsayin karen farauta domin daƙile jagororin jam’iyyun hamayya tare da jan su zuwa jam’iyya mai mulki.”

Ya ce abin da ke faruwa ba ya cikin, “manufarmu a lokacin da muka yi aiki tuƙuru domin assasa hukumar EFCC. Yanzu abubuwa na fitowa fili cewa duk wani ɗansiyasa da ke da alaƙa da jam’iyyun adawa yana fuskantar barazanar zargin cin hanci da rashawa, amma da zarar sun koma jam’iyya mai mulki, sai a ‘yafe’ musu.”

Atiku ya ce duk da cewa yaƙi da cin hanci da rashawa lamari ne da ke buƙatar goyon bayan ƴan Najeriya, ya ce haɗa yaƙin da wata manufa ta daban abu ne da ya cancanci suka daga ƙungiyoyi gwagwarmaya da ma ƙasashen duniya masu ƙawance da Najeriya.

A ƙarshe Atiku ya ce yana ba ƴan Najeriya tabbacin cewa za ba su yi shiru su zura ido suna gani ana ɗaukar matakai da suke barazana ga dimukuraɗiyyar ƙasar ba, wadda ya ce ana yunƙurin mayar da ita siyasar jam’iyya ɗaya.

benue news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuɗi dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a ƙauyuka 15 na Zamfara a mako ɗaya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huɗu ne suke biyan mafi ƙarancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp