fidelitybank

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Date:

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi na da alaƙa shigarsa cikin haɗakar jam’iyyun hamayya.

Atiku ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook, inda ya zargi gwamnatin Tinubu da yunƙurin cin zarafi da tsoratarwa da nufin murƙushe jam’iyyun hamayya a ƙasar.

“Abun da muke gani a yanzu shi ne yadda gwamnatin Tinubu ke amfani da yaƙi da cin hanci a matsayin karen farauta domin daƙile jagororin jam’iyyun hamayya tare da jan su zuwa jam’iyya mai mulki.”

Ya ce abin da ke faruwa ba ya cikin, “manufarmu a lokacin da muka yi aiki tuƙuru domin assasa hukumar EFCC. Yanzu abubuwa na fitowa fili cewa duk wani ɗansiyasa da ke da alaƙa da jam’iyyun adawa yana fuskantar barazanar zargin cin hanci da rashawa, amma da zarar sun koma jam’iyya mai mulki, sai a ‘yafe’ musu.”

Atiku ya ce duk da cewa yaƙi da cin hanci da rashawa lamari ne da ke buƙatar goyon bayan ƴan Najeriya, ya ce haɗa yaƙin da wata manufa ta daban abu ne da ya cancanci suka daga ƙungiyoyi gwagwarmaya da ma ƙasashen duniya masu ƙawance da Najeriya.

A ƙarshe Atiku ya ce yana ba ƴan Najeriya tabbacin cewa za ba su yi shiru su zura ido suna gani ana ɗaukar matakai da suke barazana ga dimukuraɗiyyar ƙasar ba, wadda ya ce ana yunƙurin mayar da ita siyasar jam’iyya ɗaya.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp