Shugaban Faransa Emmanuel Macron, ya yi gargaɗi game da furta kalaman da za su ƙara rura yakin Ukraine, kwana guda bayan da shugaba Biden ya bayyana Vladimir Putin a matsayin wanda bai kamata a bar shi ya ci gaba da mulki ba.
Macron ya shaidawa kafafen yada labaran Faransa cewa manufar ita ce tsagaita buɗe wuta a Ukraine sannan kuma a janye sojojin Rasha.
Ya ce hakan ba zai yiwu ba ta hanyar furta zafafan kalamai.
Hukumomin Amurka sun musanta cewa shugaba Biden yana nufin kiran sauyin shugabanci a Rasha a jawabinsa kan Mista Putin a ziyarar da ya kai kasar Poland.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya ce Mista Biden yana magana ne kawai kan cewa ba za a bar Mista Putin ya yi yaki da Ukraine ba.
Mista Macron ya ci gaba da tattaunawa da shugaban Rasha tun soma rikicin Ukraine.