Kotun majistare da ke filin jirgin sama na Kano ta yanke wa jaruma, Sadiya Haruna, hukuncin zaman watanni shida a gidan gyaran hali.
Alkali Muntari Garba Dandago ne ya yanke mata wannan hukuncin a kan kalaman batanci da cin zarafi da ta rinka yi a kan mawaki kuma jarumi Isah A. Isah.
A shekaru biyu da suka gabata ne hargitsi ya rincabe tsakanin Sadiya Haruna da Isah, wanda tsohon saurayin ta ne, ta ce, sun yi auren mutu’a.
Kotu ta yanke wa jarumar Kannywood kuma mai siyar da kayan mata da maza, mai suna Sadiya Haruna hukuncin zaman wata shida a gidan yari ba tare da zabin tara ba. An samu Sadiyan da laifin bata sunan wani jarumi kuma mawakin kannywood mai suna Isa A Isa,