Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa, bayyana takaici da barazanar da Gwamna Nasir el-Rufai na jihar Kaduna ya yi na gayyatar sojojin haya daga kasashen waje domin yakar ta’addancin cikin gida wani karin tabbaci ne da kuma amincewa da gazawar jam’iyyar APC.
A wata sanarwa da Debo Ologunagba, sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP ya fitar, ya dage cewa el-Rufai ba zai iya nisantar da kansa daga masu rura wutar rikicin tsaro da taimakawa wadanda ta ce ta koma ayyukan ta’addanci da suka addabi kasar a yau.
Jam’iyyar PDP ta kalubalanci El-Rufai da sauran jiga-jigan jam’iyyar APC da su tofa albarkacin bakinsu kan ikirari da wani tsohon jigo a jam’iyyar APC ya yi cewa shugabannin jam’iyyar ne suka kawo ‘yan ta’addan da suke wawure al’ummar kasar, domin yin magudi a zaben 2019 mai zuwa.
Don haka ta shaida wa Gwamna el-Rufai cewa, barazanar da ya yi na shigo da sojojin haya daga kasashen waje ba ta da amfani, kuma tana iya kara tabarbarewar yanayin tsaro a kasar nan.