fidelitybank

Kalaman Ƙabilanci: Atiku ya shiga tsaka mai wuya gabanin zaɓen 2023

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya sha suka sakamakon shawarar da ya baiwa ‘yan Arewa gabanin zaben 2023.

Atiku ya bayyana haka ne a wani taron da aka gudanar a Kaduna, inda ya bayyana cewa, “Abin da talakawan Arewa ke bukata shi ne wanda ya fito daga Arewa kuma ya fahimci wani bangare na kasar nan kuma ya iya gina gadoji a fadin kasar nan.

“Wannan shi ne abin da dan Arewa yake bukata, ba ya bukatar dan takarar Yarbawa ko Igbo, na tsaya a gabanka a matsayina na dan Najeriya dan asalin Arewa.”

Da take mayar da martani, Ohanaeze Ndigbo, a wata sanarwa a ranar Lahadi ta hannun babban sakatarenta, Mazi Okechukwu Isiguzoro, ta ce ta bakin Atiku, ya gama duk abin da ya rage na PDP.

“Mun ga yana da ban mamaki da ban takaici a ce dattijon jiha kuma dan takarar shugaban kasa, a matsayin wanda ya taba zama mataimakin shugaban kasa a Najeriya sau daya zai iya hawa mumbari a wani taron jama’a ya faɗi irin wannan kalaman na kabilanci.

“Muna cikin damuwa cewa a irin wannan lokaci Najeriya na neman hadin kan kasa, Atiku yana kara jefa kasar cikin rugujewa; ya nuna cewa bai da karfin jagoranci da hada kan kasar nan.

“Tuni burinsa ya ruguza jam’iyyar PDP ya kuma tura ta daga lamba daya zuwa uku idan ba karfi na hudu ba. Yanzu dai yana son ya kawo rarrabuwar kawuna a cikin harkokin kasar. Muna rokon ‘yan Najeriya su ce a’a ta hanyar kin shi da kakkausan harshe a rumfunan zabe,” inji Ohanaeze.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp