Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal da tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Honarabul Yakubu Dogara a ranar Asabar sun gana da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike a Fatakwal.
An gudanar da taron sirrin ne a gidan gwamna Wike da ke Rumueprikom, karamar hukumar Obio-Akpor ta jihar Ribas.
Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, Dogara ya dangana ziyarar ta su ne kan neman gina Najeriya mai dunkulewa.
“Kowa ya yarda da mu cewa, Gwamna Wike na daya daga cikin shugabannin siyasa da ba makawa. A gare mu, neman gina Najeriya ce mai dunkulewa. Don haka, muna jin cewa a matsayin wani ɓangare na tsarin ajandar, ya kamata mu sadu da shi kuma shine dalilin da ya sa muke nan. Kuma ga sauran, ko da yake, watakila nan gaba za mu iya tattauna hakan. “
Hakazalika, tsohon sakataren gwamnatin tarayya Lawsl ya bayyana cewa, ziyarar ta su ita ce ziyarar ‘yan uwantaka da gwamnan jihar Ribas.
“Mun zo ziyarar ɗan’uwanmu. Shi (Wike) dan uwanmu ne. Don haka, a yanzu da kuma, Littafi Mai Tsarki ya umurce ku ku ziyarci juna. Abin da muka yi ke nan.”
Lawal ya ce, hulda da Wike ba ta da alaka da taron da wasu shugabannin Arewa suka yi a Abuja ranar Juma’a.
“A’a, akwai abubuwa da yawa da a duniya kuke buƙatar ziyartar ɗan’uwa, don haka babu ruwanmu da taron da muka yi a Abuja.”