fidelitybank

Kakakin majalisa da tsohon sakataren Gwamnati sun ziyarci Wike

Date:

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal da tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Honarabul Yakubu Dogara a ranar Asabar sun gana da gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike a Fatakwal.

An gudanar da taron sirrin ne a gidan gwamna Wike da ke Rumueprikom, karamar hukumar Obio-Akpor ta jihar Ribas.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron, Dogara ya dangana ziyarar ta su ne kan neman gina Najeriya mai dunkulewa.

“Kowa ya yarda da mu cewa, Gwamna Wike na daya daga cikin shugabannin siyasa da ba makawa. A gare mu, neman gina Najeriya ce mai dunkulewa. Don haka, muna jin cewa a matsayin wani ɓangare na tsarin ajandar, ya kamata mu sadu da shi kuma shine dalilin da ya sa muke nan. Kuma ga sauran, ko da yake, watakila nan gaba za mu iya tattauna hakan. “

Hakazalika, tsohon sakataren gwamnatin tarayya Lawsl ya bayyana cewa, ziyarar ta su ita ce ziyarar ‘yan uwantaka da gwamnan jihar Ribas.

“Mun zo ziyarar ɗan’uwanmu. Shi (Wike) dan uwanmu ne. Don haka, a yanzu da kuma, Littafi Mai Tsarki ya umurce ku ku ziyarci juna. Abin da muka yi ke nan.”

Lawal ya ce, hulda da Wike ba ta da alaka da taron da wasu shugabannin Arewa suka yi a Abuja ranar Juma’a.

“A’a, akwai abubuwa da yawa da a duniya kuke buƙatar ziyartar ɗan’uwa, don haka babu ruwanmu da taron da muka yi a Abuja.”

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp