fidelitybank

Kafin Buhari ya sauka zan bude matatar man fetur – Dangote

Date:

Shugaban rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, a jiya ya bada tabbacin cewa, matatar man Dangote zata fara aiki kafin shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar mulki a shekarar 2023.

Ya bayyana hakan ne ga manema labarai na fadar shugaban kasa bayan ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Da aka tambaye shi ko yaushe matatar man za ta fara aiki, babban attajirin Afrika ya ce; “Da yardar Allah, Shugaban kasa zai zo ya kaddamar da aikin kafin karshen wa’adinsa.”

A cewarsa, idan matatar ta fara aiki, matatar za ta samar da ayyukan yi tare da samar da karin kudaden haraji wanda gwamnati za ta yi amfani da su wajen bunkasa kasar.

“A nan gaba kadan ana sa ran za su ga karin ayyukan yi, ana sa ran za su kara samun wadata. Muna ci gaba da yin sabbin abubuwa da abubuwa masu kyau, sannan kuma muna ci gaba da biyan harajin da za su taimaka wa kokarin gwamnati na samar da ilimi da lafiya da sauran su,” inji shi.

Da aka tambaye shi ko ya damu da karancin potassium a sakamakon rikicin Rasha da Ukraine, Dangote ya ce, babu bukatar damuwa domin kashi 26% na arzikin da ake samu a duniya ya fito ne daga kasashen biyu.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp