Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Mahmood Yakubu, ya ce, nan da kafin watanni 10 hukumar za ta fitar da ka’idoji dokar zaben 2023.
Za a fara zaben ne a watan Fabrairun 2023, wanda ke nuni da cewa INEC na shirin fitar da ka’idojin kafin karshen watan Afrilu.
Hakan na kunshe ne a cikin jaridar Daily Bulletin ta INEC da ta fitar ranar Talata.
Yakubu ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakwancin wata tawaga daga gidauniyar John D da Catherine T. MacArthur Foundation, a Abuja.
Shugaban na INEC ya tunatar da cewa, a shekarar 2019, hukumar ta takura da lokaci saboda rashin tabbas da ya biyo bayan tsarin dokar zabe.
Ya ce, hakan ya sa hukumar ta sanya hannu kan ka’idoji a ranar 19 ga Janairu, 2019, makonni kadan kafin zaben.
“Amma muna fatan cewa, a wannan karon za mu sanya hannu kan ka’idoji akalla watanni 10 kafin babban zabe na gaba, wanda hakan ke da kyau a gare mu.”
Da yake karin haske game da tushen ikon hukumar na samar da ka’idoji Shugaban INEC ya ce, hukumar ta yi farin ciki da amincewar shugaban kasa Muhammadu Buhari kan dokar zabe.