fidelitybank

Kafar yaɗa labarai ta ABC za ta biya Trump diyar dala miliyan 15

Date:

Kafar yaɗa labarai ta ABC News da ke Amurka ta amince ta biya dala miliyan 15 ga sabon shugaban Amurka mai jiran-gado, Donald Trump bayan da ya kai kafar ƙara a kan zargin ɓata masa suna.

Ya kai ƙarar ne saboda wata hira da mai gabatar da shiri a tashar, George Stephanopoulos, yake cewa an samu shugaban mai jiran-gado da laifin fyade a wata shari’a.

A lokacin wata hira a shirin na talabijin, a watan Maris, hirar da ta yi zafi, inda, George Stephanopoulos da ke tattaunawa da ‘yar majalisar wakilai ta jamiyyar Republican, mai gabatarwar ya rika cewa kotu ta samu Mista Trump da laifin fyaɗe.

Mista Trump ya kai karar tashar talabijin ɗin ta ABC da kuma Mista Stephanopoulos.

Yanzu dai bayanai na nuna cewa ɓangarorin biyu sun sasanta, kuma a ƙarƙashin yarjejeniyar da suka cimma, ABC za ta biya dala miliyan 15, ga wata gidauniyar Trump da kuma wani gidan adana kayan tarihi.

Haka kuma kafar yaɗa labaran za ta biya dala miliyan ɗaya da Mista Trump ɗin ya kashe a sharia’r.

Bugu da ƙari a ƙarƙashin yarjejeniyar sasanton za a sanya wata sanarwa a jikin wata Maƙala da ake rubutawa a shafin intanet na ABC News da ke nuna kafar da George Stephanopoulos na nadamar kalaman da ya yi.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp