fidelitybank

Kafar yaɗa labarai ta ABC za ta biya Trump diyar dala miliyan 15

Date:

Kafar yaɗa labarai ta ABC News da ke Amurka ta amince ta biya dala miliyan 15 ga sabon shugaban Amurka mai jiran-gado, Donald Trump bayan da ya kai kafar ƙara a kan zargin ɓata masa suna.

Ya kai ƙarar ne saboda wata hira da mai gabatar da shiri a tashar, George Stephanopoulos, yake cewa an samu shugaban mai jiran-gado da laifin fyade a wata shari’a.

A lokacin wata hira a shirin na talabijin, a watan Maris, hirar da ta yi zafi, inda, George Stephanopoulos da ke tattaunawa da ‘yar majalisar wakilai ta jamiyyar Republican, mai gabatarwar ya rika cewa kotu ta samu Mista Trump da laifin fyaɗe.

Mista Trump ya kai karar tashar talabijin ɗin ta ABC da kuma Mista Stephanopoulos.

Yanzu dai bayanai na nuna cewa ɓangarorin biyu sun sasanta, kuma a ƙarƙashin yarjejeniyar da suka cimma, ABC za ta biya dala miliyan 15, ga wata gidauniyar Trump da kuma wani gidan adana kayan tarihi.

Haka kuma kafar yaɗa labaran za ta biya dala miliyan ɗaya da Mista Trump ɗin ya kashe a sharia’r.

Bugu da ƙari a ƙarƙashin yarjejeniyar sasanton za a sanya wata sanarwa a jikin wata Maƙala da ake rubutawa a shafin intanet na ABC News da ke nuna kafar da George Stephanopoulos na nadamar kalaman da ya yi.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp