Tsohon gwamnan Jihar Legas, Bola Tinubu, ya ce, kafafen sada zumunta sun sauya masa maganar sa wadda ya yi a baya cewa, ya shirya yin artabu da kowa, domin burinsa na zama shugaban kasa ya tabbata.
Hadimin Tinubu na harkokin kafafen sada zumunta, Tunde Rahman ne ya bayyana hakan ta wata takarda wadda ya fitar a ranar Litinin.
Ya ce, ya yi amfani da karin maganan da ke cewa, idan za ka yi dambe da alade sai ka shirya yin datti.
Takardar ta kara da cewa, an sauya wa jagoran APC din maganarsa, wadda ya ce, ya lashi takobin yin kaca-kaca da duk wanda ke neman dakatar da cikar burin sa na takarar shugaban kasa a 2023.
A cewarsa: “Rahoton ba daidai bane kuma, akwai kuskure a cikinsa. Abin ban takaici shi ne yadda ‘yan jaridu da jama’a suka dinga caccaka suna suka ta. Abin ban takaici ne maganganun sa aka dinga saboda an sauya magana ta. Hakan yasa na yi wannan karin bayanin.”