Jam’iyyar PDP ta ce, shugabacin jam’iyyar da ke biyayya ga tsohon gwamnan jihar Ribas Nyesom Wike, ta sani a matsayin shugabanin jam’iyyar a jihar ta Ribas.
Jam’iyyar ta PDP ta ce, duk da cewar an ɗaukaka ƙara kan hukuncin da kotu ta yi na sauke shugabanin jam’iyyar da ke Ribas, da ke biyyaya ga tsohon gwaman jihar, bai kamata ɓangaren gwamnan jihar su kafa wani shugabancin riƙon ƙwarya ba, kamata ya yi kowa ya dakata a jira hukucin kotu na gaba.
Mataimakin kakakin jam’iyyar PDP na ƙasa, Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana haka, inda ya ce kotun na gaba ne zai warware duk wani ƙullin da ke tattare da rikicin shugabancin jihar.
Tun da farko dai, wata kotu ce ta rushe shugabannin jam’iyyar masu bibiya ga ministan Abuja, Nyesome Wike, wanda hakan ya sa ƴaƴan jam’iyyar na ɓangaren gwamnan jihar na yanzu, Simi Fubara suka sanar da kafa shugabancin riƙon ƙwarya.