‘Yan ta’adda sun sake yin garkuwa da mutane Biyar a yankin Dallatu da kasuwar Da’a a Dutsen Abba da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna.
Lamarin na faruwa ne bayan sa’o’i 24 da ‘yan bindigar su ka tare hanyar Kaduna zuwa Zariya tare da kashe mutane Uku tare da yin awon gaba da mutane da dama.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna har yanzu ba ta mayar da martani ga rahoton harin da a ka kai wa al’umomin biyu ba, sai dai mazauna garin sun ce ‘yan bindigar da su ka kai farmaki kauyen Dallatu da misalin karfe 1:00 na ranar Laraba, sun yi garkuwa da mutane Biyu tare da wuce kauyen Kasuwar Da’a inda suka yi awon gaba da wasu Shida daga cikinsu.
Sai dai majiyar ta shaida wa Aminiya cewa an sako yaran Uku da safiyar Laraba, inda a ka yi garkuwa da mutane Biyar.
Wasu ‘yan ta’adda sun kai farmaki kan masu ababen hawa da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya a wani samame da suka kwashe kusan sa’o’i uku ana yi tare da salwantar da rayukan matafiya uku.