Gwamna David Umahi ya bukaci mazauna jihar Ebonyi da na Ndigbo baki daya da su zabi Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa.
Gwamnan ya yi wannan kiran ne a wajen kaddamar da yakin neman zaben kananan hukumomin jam’iyya mai mulki a Iboko, hedikwatar karamar hukumar Izzi, inji rahoton jaridar The Nation.
Gwamna Umahi ya ce, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC yana kaunar al’ummar Igbo, inda ya kara da cewa kabilar Igbo za ta samu cikakkiyar matsuguni tare da daukar nauyinta idan Tinubu ya zama shugaban kasa.
Ya bayyana Tinubu a matsayin gogaggen shugaba kuma hazikin shugaba wanda ke da karfin da zai kai kasar nan zuwa mataki na gaba. “Dole ne mu koma rumfunan zaben mu. Muna tare da Tinubu da Shettima. Zasu kula da jihar Ebonyi yadda Buhari ya dauki nauyin jihar Ebonyi. Yadda Buhari yake kula da mu shine yadda Jagaban zai kula da Ndigbo.
“Jagaban ya kasance gwamnan jihar Legas kuma a karkashinsa, Ndigbo a Legas ya ci gaba kuma har yanzu suna ci gaba. Ba a yi mana ja-gora ba; za mu bi mutumin da ya san hanya,” in ji Umahi.