fidelitybank

Ka sauka daga mulki kaiwa Buhari ka gaza – Ƙungiyar Dattawan Arewa

Date:

Ƙungiyar Dattawan Arewa ta Northern Elders Forum (NEF) ta nemi Shugban Ƙasa Muhammadu Buhari da ya sauka daga mulki nan take, sakamakon kashe-kashen da ake fama da su a faɗin ƙasar, musamman a arewaci.

Da yake magana cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, kakakin ƙungiyar Hakeem Baba-Ahmed, ya ce,Buhari “ba zai iya kawo ƙarshen matsalar tsaro da ta addabe mu ba”.

“Da alama gwamnatin Buhari ba ta da abin cewa game da ƙalubalen tsaro da muke ciki. Ba zai yiwu mu ci gaba da zama ƙarƙashin ikon masu kisa ba, da masu garkuwa da mutane, da masu fyaɗe, da miyagun da suka hana mu ‘yancinmu na zama lafiya,” a cewar ƙungiyar.

Kiran nasu na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan ‘yan bindiga sun kashe kusan mutum 200 a Jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya, da kuma sace wasu ɗaliban kwaleji mata da aka yi a Jihar Zamfara ranar Talata da dare.

Kazalika, har yanzu ‘yan bindigar da suka kai hari kan jirgin ƙasa na Kaduna-Abuja na riƙe da gwamman matafiyan da suka yi garkuwa da su, inda suke neman gwamnatin Buhari ta biya musu “buƙatunsu”.

“Kundin tsarin mulkinmu ya tanadi yadda shugabanninmu za su sauka daga mulki idan suka gaza ko kuma saboda wani dalili na ƙashin-kai,” in ji NEF. “Loƙaci ya yi da ya kamata Buhari ya fara tunanin wannan zaɓin.”

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp