fidelitybank

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Date:

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu Shinkafi, ya caccaki kakakin gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, Mustapha Ja’afaru Kaura, bisa zarginsa da yin tsokaci a kan karamin ministan tsaro, Bello Matawalle da Sanata AbdulAzeez Yari.

Shinkafi ya baiwa kakakin wa’adin kwanaki bakwai da ya fito fili ya nemi afuwa a rubuce ko kuma ya fuskanci shari’a.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da jaridar DAILY POST a Kaduna a ranar Lahadi, dan gwagwarmayar ya ce, “Ba za mu dunkule hannunmu mu kalli yadda mai magana da yawun gwamnan ke zagin ‘yan jahohinmu da suka yi gwamna a jihar kuma har yanzu suna yi wa kasa hidima a mukamai daban-daban.

“Ya kamata (kakaki) ya mika uzurinsa a rubuce cikin kwanaki bakwai ko kuma a hukunta shi, kuma na yi imanin cewa gwamnan bai aike shi ya aikata irin wannan mummunan abu a kan manyan mutanen jihar guda biyu ba, haka kuma gwamnan da na sani sosai ba zai taba fitowa fili ya caccaki manyan gwamnonin jihar ba kamar yadda Mustapha Ja’afaru Kaura ya yi.

“Kisan hali ne kawai kuma ba za mu bar irin wannan aiki ya ci gaba da kasancewa a cikin jihar ba.”

Shinkafi ya lura cewa abin da kakakin ya yi abu ne da ba za a amince da shi ba a cikin al’umma mai wayewa, yana mai jaddada cewa ya kamata a mutunta dattawa saboda suna da kima ga al’umma kuma suna yin abubuwa da yawa don inganta rayuwar jama’a a jihar.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp