fidelitybank

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Date:

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu Shinkafi, ya caccaki kakakin gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, Mustapha Ja’afaru Kaura, bisa zarginsa da yin tsokaci a kan karamin ministan tsaro, Bello Matawalle da Sanata AbdulAzeez Yari.

Shinkafi ya baiwa kakakin wa’adin kwanaki bakwai da ya fito fili ya nemi afuwa a rubuce ko kuma ya fuskanci shari’a.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da jaridar DAILY POST a Kaduna a ranar Lahadi, dan gwagwarmayar ya ce, “Ba za mu dunkule hannunmu mu kalli yadda mai magana da yawun gwamnan ke zagin ‘yan jahohinmu da suka yi gwamna a jihar kuma har yanzu suna yi wa kasa hidima a mukamai daban-daban.

“Ya kamata (kakaki) ya mika uzurinsa a rubuce cikin kwanaki bakwai ko kuma a hukunta shi, kuma na yi imanin cewa gwamnan bai aike shi ya aikata irin wannan mummunan abu a kan manyan mutanen jihar guda biyu ba, haka kuma gwamnan da na sani sosai ba zai taba fitowa fili ya caccaki manyan gwamnonin jihar ba kamar yadda Mustapha Ja’afaru Kaura ya yi.

“Kisan hali ne kawai kuma ba za mu bar irin wannan aiki ya ci gaba da kasancewa a cikin jihar ba.”

Shinkafi ya lura cewa abin da kakakin ya yi abu ne da ba za a amince da shi ba a cikin al’umma mai wayewa, yana mai jaddada cewa ya kamata a mutunta dattawa saboda suna da kima ga al’umma kuma suna yin abubuwa da yawa don inganta rayuwar jama’a a jihar.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp