Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma’a da Liitnin masu zuwa a matsayin ranakun hutu ga ma’aikatan ƙasar domin bikin Babbar Sallah.
Ranakun za su dace da 6 da kuma 9 ga watan Yuni da muke ciki.
Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hutun a madadin gwamnatin tarayya, yana mai taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar bikin.
A ranar Juma’a 6 ga watan Yuni ne Musulmi za su gudanar da Idin Babbar Sallar, wanda ya ƙunshi yanka dabbobin layya.