fidelitybank

Jonathan ya ƙalubalanci ƴan takarar shugaban ƙasa

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci daukacin ‘yan takara a zaben 2023 da suka hada da irin su Peter Obi, Atiku Abubakar, da Bola Tinubu, da dai sauran su da su yi kokarin ganin yakin neman zabensu ya kasance mai tsafta kuma babu tashin hankali.

Jonathan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na fatan alheri da aka karanta a Abuja a wajen rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa kan zaben 2023 na farko, wanda ya samu halartar ‘yan takarar shugaban kasa da jam’iyyunsu.

Ya kuma yi kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi ‘yan Najeriya.

Jonathan ya ce, “Muna kan wani muhimmin mataki a rayuwarmu ta kasa inda ba mu da wani zabi illa inganta hadin kan kasa, soyayya da fata domin samun ci gaban da ake bukata.

“Ba za mu iya ci gaba da wasa da siyasar ɗaci da rarrabuwar kawuna ta kabilanci da addini ba. Domin irin wannan siyasar tana nuna babban hatsari ga hadin kanmu, ci gabanmu da wadatar dimokuradiyyarmu.

“Dole ne mu yi la’akari da illar kalaman kyama, labaran karya da farfaganda marasa tunani, musamman a wani yanayi da ya kamata a karfafa tsarin hadin kai da kwanciyar hankali.

“Ina kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da neman gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi jama’armu.

“Ya kamata, ta kowane hali, su guje wa hare-haren da ba dole ba a kan mutane, da kuma amfani da kalaman batanci ga wadancan abubuwan da ke haifar da hargitsi da rikici a lokacin zabe.”

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp