fidelitybank

Jonathan ya ƙalubalanci ƴan takarar shugaban ƙasa

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci daukacin ‘yan takara a zaben 2023 da suka hada da irin su Peter Obi, Atiku Abubakar, da Bola Tinubu, da dai sauran su da su yi kokarin ganin yakin neman zabensu ya kasance mai tsafta kuma babu tashin hankali.

Jonathan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na fatan alheri da aka karanta a Abuja a wajen rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa kan zaben 2023 na farko, wanda ya samu halartar ‘yan takarar shugaban kasa da jam’iyyunsu.

Ya kuma yi kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi ‘yan Najeriya.

Jonathan ya ce, “Muna kan wani muhimmin mataki a rayuwarmu ta kasa inda ba mu da wani zabi illa inganta hadin kan kasa, soyayya da fata domin samun ci gaban da ake bukata.

“Ba za mu iya ci gaba da wasa da siyasar ɗaci da rarrabuwar kawuna ta kabilanci da addini ba. Domin irin wannan siyasar tana nuna babban hatsari ga hadin kanmu, ci gabanmu da wadatar dimokuradiyyarmu.

“Dole ne mu yi la’akari da illar kalaman kyama, labaran karya da farfaganda marasa tunani, musamman a wani yanayi da ya kamata a karfafa tsarin hadin kai da kwanciyar hankali.

“Ina kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da neman gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi jama’armu.

“Ya kamata, ta kowane hali, su guje wa hare-haren da ba dole ba a kan mutane, da kuma amfani da kalaman batanci ga wadancan abubuwan da ke haifar da hargitsi da rikici a lokacin zabe.”

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp