fidelitybank

Jonathan ya ƙalubalanci ƴan takarar shugaban ƙasa

Date:

A ranar Alhamis din da ta gabata ne tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci daukacin ‘yan takara a zaben 2023 da suka hada da irin su Peter Obi, Atiku Abubakar, da Bola Tinubu, da dai sauran su da su yi kokarin ganin yakin neman zabensu ya kasance mai tsafta kuma babu tashin hankali.

Jonathan ya yi wannan kiran ne a sakon sa na fatan alheri da aka karanta a Abuja a wajen rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ta kasa kan zaben 2023 na farko, wanda ya samu halartar ‘yan takarar shugaban kasa da jam’iyyunsu.

Ya kuma yi kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi ‘yan Najeriya.

Jonathan ya ce, “Muna kan wani muhimmin mataki a rayuwarmu ta kasa inda ba mu da wani zabi illa inganta hadin kan kasa, soyayya da fata domin samun ci gaban da ake bukata.

“Ba za mu iya ci gaba da wasa da siyasar ɗaci da rarrabuwar kawuna ta kabilanci da addini ba. Domin irin wannan siyasar tana nuna babban hatsari ga hadin kanmu, ci gabanmu da wadatar dimokuradiyyarmu.

“Dole ne mu yi la’akari da illar kalaman kyama, labaran karya da farfaganda marasa tunani, musamman a wani yanayi da ya kamata a karfafa tsarin hadin kai da kwanciyar hankali.

“Ina kira ga ’yan takara da masu tallata su da magoya bayansu da su jajirce tare da neman gudanar da yakin neman zabensu kan batutuwan da suka shafi jama’armu.

“Ya kamata, ta kowane hali, su guje wa hare-haren da ba dole ba a kan mutane, da kuma amfani da kalaman batanci ga wadancan abubuwan da ke haifar da hargitsi da rikici a lokacin zabe.”

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp