A daidai lokacin da watan azumi ke ci gaba da nitsawa, jihohin Najeriya guda bakwai sun ware tsabar kudi har naira biliyan 28.3 domin ciyar da masu azumi a watan na Ramadan, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.
Jihohin guda bakwai sun hada da Katsina da Sokoto da Kano da Jigawa da Kebbi da Naija da kuma Kebbi.
Bayanai sun nuna cewa akwai wasu karin jihohin arewacin da dama da su ma suka ware kudaden domin ciyarwa duk da cewa dai ba su bayyana a fili ba.
Wannan abu dai ya janyo kace-na-ce a tsakanin al’umma inda wasu malaman addinin ke kiraye-kirayen da a yi bincike bisa lura da irin yawan kudaden da aka ware din.
Jihar Katsina ce dai ta fi kowacce jiha a yawan kudin ciyarwar inda ta ware naira biliyan 10.
Sai kuma jihar Sokoto da ke biye mata da naira biliyan 6.7, sannan jihar Kano kuma ta fitar da naira biliyan shida.
Ita kuwa jihar Jigawa ta fitar da naira biliyan 2.83, sai jihar Kebbi da ta fitar da naira 1.5 biliyan.
Jihar Naija ta ware naira miliyan 976, inda jihar Yobe ita kuma ta ware naira miliyan 178 domin ciyarwar.
Katsina State topped the chart for the feeding programme by budgeting N10 billion.