fidelitybank

Jirgin yaƙin ruwan Birtaniya na taya Najeriya yaƙi – Hukuma

Date:

Wani jirgin ruwan yaƙin Birtaniya, HMS Trent, ya sauka a Lagos don taimakawa wajen yaƙi da haramtattun ayyuka ciki har da fashin teku da fasa-ƙwauri a tsakanin ƙasashen yankin.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriya ya fitar, ta ce wannan karo na biyu da jirgin yaƙin Trent ke kawo ziyara Najeriya.

“Ziyarar za ta taimaka wajen bunƙasa samar da horo da tallafa wa tsaron teku a yankin mashigin tekun Guinea,” kamar yadda sanarwar ta ce.

Jirgin HMS Trent ya baro Gibraltar ɗauke da wani rukunin ƙwararrun sojojin ƙundumbalar Birtaniya da wani jirgi maras matuƙi da ke aikin tattara bayanai mai suna Puma. Aikin jirgin HMS Trent shi ne ya tallafa wa Ƙasashen Afirka ta Yamma abokan ƙawancen Birtaniya wajen inganta ƙwazo kan yaƙi da laifuka a teku da kuma tabbatar da kawo ƙarin kwanciyar hankali a faɗin yankin.

Da harkokin kasuwancin fam biliyan shida na Birtaniya da ke wucewa ta yankin, wani ɓangare na aikin Trent shi ne tallafa wa ayyukan kwanciyar hankali a Mashigin Tekun Guinea ta hanyar ba da horo don taimaka wa rundunonin sojin ruwan ƙasashe abokan ƙawance, su kai yaƙi ga masu aikata laifi da kyautata ƙawance da musayar ilmi a lokacin da suke sintiri don ƙara tabbatar da tsaro.

Babban kwamandan jirgin ruwan HMS Trent, Kwamanda Tim Langford, ya ce, “wata karramawa ce ga jirgin yaƙin HMS TRENT ya sake komo wa Najeriya, wannan wata muhimmiyar ziyara ce ga aikin da aka turo jirgin ruwan zuwa Afirka ta Yamma tsawon wata uku”.

Mataimakin Babban Jakadan Birtaniya a Najeriya, Jonny Baxter ya ce, “Turo wannan jirgin ruwan yaƙi zuwa Afirka ta Yamma wata manuniya ce kan yadda Birtaniya ke daɗa bayar da himma a matakin harkokin duniya wajen shawo kan ƙalubalen tsaro.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp