fidelitybank

Jirgin Sojan sama ne ya kai ɗauki inda ƴan ta’adda suka kai hari – Gwamnatin Kaduna

Date:

Gwamnatin Jihar Kaduna ta musanta rahotannin da ke cewa, ‘yan fashin daji sun kai hare-hare tare da taimakon wani jirgi mai saukar ungulu, tana mai tabbatar da mutuwar mutum 32.

Tun farko shugaban ƙungiyar tuntuɓa ta ‘yan ƙabilar Adara (ADA) da kuma mai magana da yawun shugaban ƙungiyar mazauna Kudancin Kaduna ta SOKAPU sun faɗa cikin wata sanarwa cewa wani jirgin helikwafta ne ya taimaka wa ‘yan fashin dajin yayin hare-haren. In ji BBC.

Sai dai cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Alhamis, Kwamashinan Tsaro Samuel Aruwan ya musanta rahoton yana mai cewa, jirgin da aka gani na rundunar sojan Najeriya ne da ya kai ɗauki wurin.

Sai dai kwamashinan ya tabbatar da kashe mutum 31 a garuruwan Dogon Noma da Unguwan Sarki, sannan maharan suka kashe mutum ɗaya a Unguwan Maikori tare da ƙona gidaje a ranar Lahadi da ta wuce.

“Zuwan jirgin soja na rundunar Operation Whirl Punch ne ya daƙile yunƙurin ‘yan fashin bayan sun kashe mutum ɗaya tare da ƙona gidaje. Saboda haka labarin cewa jirgi ya taimaka wa ‘yan fashi ba gaskiya ba ne,” a cewarsa.

Kazalika, kwamashinan ya nemi waɗanda suke iƙirarin da su kawo wa gwamnati “hujjar yankan shakku”.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp