Wani jirgin dakon kaya na kamfanin Allied Air, ya yi hatsari a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake NAIA a Abuja ranar Laraba.
Lamarin ya faru ne sakamakon gazawar daya daga cikin na’urorin saukar jirgin.
Zagazola Makama, kwararre kan yaki da ta’addanci da tayar da kayar baya a tafkin Chadi, wanda ya bayyana hakan a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Laraba, ya bayyana cewa jirgin na dauke da ma’aikata shida ne.
Makama ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba saboda an kwashe ma’aikatan cikin gaggawa.
Ya bayyana cewa a halin yanzu ma’aikatan na ci gaba da duba lafiyarsu a sashin lafiya na 063 na sojojin saman Najeriya (NAF).
“Masu bayar da agajin gaggawa sun yi gaggawar tabbatar da tsaron wurin da hatsarin ya faru, inda suka killace wurin a karkashin kulawar kwamandan filin jirgin sama na sojoji (MAC) da sauran hukumomin da abin ya shafa.
“Lamarin ya haifar da rufe titin jirgin na wucin gadi, wanda ya haifar da tsaiko ga zirga-zirgar jiragen sama da masu fita. An shawarci fasinjoji da kamfanonin jiragen sama da su yi tsammanin kawo cikas har sai an samu sanarwa.
“Hukumomin filin jirgin sama da hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya NCAA na ci gaba da kokarin cire nakasassun jiragen da kuma duba titin saukar jiragen domin samun barna. Jami’ai suna aiki don dawo da ayyukan yau da kullun cikin sauri.
“Za a samar da Æ™arin sabuntawa yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin,” in ji masanin tsaro.