Ma’aikatar kula da harkokin sufuri a Kamaru ta ce, wani karamin jirgin saman fasinja da ke ɗauke da mutum 11 ya yi hadari a wani daji da ke kudu da Yaounde babban birnin Kamaru a jiya Laraba.
Har yanzu ba a san musababbanin abin da ya haddasa hadarin ba, to amma rahotannin sun ce sadarwa ta katse tsakanin filin jirgin da kuma matuƙan jirgin.
Daga bisani an gano shi a kusa da wani daji da ke kusa da Nanga Eboko da ke da nisan kilomita 150 daga Yaounde.
Jirgin ya tashi ne daga filin jirgin saman Nsimalen zuwa Belabo da ke gabashin kasar in ji ma’aikatar sufurin.
Kamfanin dillancin labarai na AFP, ya ruwaito cewa wani kafanin Mai mai zaman kansa mai suna COTCO ne ya yi shatar jirgin.
Wannan ne dai karo na farko da aka samu babban hadarin jirgin sama a kasar tun shekarar 2007, a lokacin da jirgin saman Kenya dauke d afasinjoji 114 ya yi hadari jim kadan bayan ya tashi da ga Douala.