fidelitybank

Jirgin sama ya yi hadari a Kamaru

Date:

Ma’aikatar kula da harkokin sufuri a Kamaru ta ce, wani karamin jirgin saman fasinja da ke ɗauke da mutum 11 ya yi hadari a wani daji da ke kudu da Yaounde babban birnin Kamaru a jiya Laraba.

Har yanzu ba a san musababbanin abin da ya haddasa hadarin ba, to amma rahotannin sun ce sadarwa ta katse tsakanin filin jirgin da kuma matuƙan jirgin.

Daga bisani an gano shi a kusa da wani daji da ke kusa da Nanga Eboko da ke da nisan kilomita 150 daga Yaounde.

Jirgin ya tashi ne daga filin jirgin saman Nsimalen zuwa Belabo da ke gabashin kasar in ji ma’aikatar sufurin.

Kamfanin dillancin labarai na AFP, ya ruwaito cewa wani kafanin Mai mai zaman kansa mai suna COTCO ne ya yi shatar jirgin.

Wannan ne dai karo na farko da aka samu babban hadarin jirgin sama a kasar tun shekarar 2007, a lokacin da jirgin saman Kenya dauke d afasinjoji 114 ya yi hadari jim kadan bayan ya tashi da ga Douala.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp