Hukumar binciken hadurra ta (AIB) ta bayyana cewa, adadin rayukan mutane 2,038 ne suka rasa ransu a hadarurrukan jiragen sama a Najeriya tsakanin shekarar 1969 zuwa 2022
Kwamishinan AIB, Akin Olateru ne ya bayyana hakan a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da yake jawabi ga iyalan wadanda hadarin jirgin sama ya rutsa da a Abuja.
Ya bayyana cewa, fasinjoji 1,996 ne suka bata a cikin jirgin, yayin da wasu 42 suka mutu a kasa.
Olateru ya ce, matakan da hukumar ta fara, sun haifar da raguwar yawan hadurran jiragen sama a kasar nan.
Ya kuma ce, “Rashin kula da lafiyar jiragen sama, ba wai kawai ya lalata jirgin da abin ya shafa ba ne, har ma ya na iya haifar da asarar rayukan mutane da za a iya kaucewa a cikin jirgin da ba sa so, wani lokacin kuma a kasa.”