Kamfanin jiragin sama na AZMAN Air da ke jigilar fasinjoji daga Saudiyya zuwa Najeriya ya kama da wuta
Wata majiya mai tushe ta shaida wa jaridar Leadership cewa, jirgin na shirin barin Jeddah ne a kasar Saudiyya lokacin da lamarin ya faru.
Majiyoyi sun bayyana cewa, jirgin ya shirya jigilar fasinjoji sama da 120 da aka ce, zai tashi da misalin karfe 10 na daren Alhamis.
Majiyar ta bayyana cewa matukin jirgin ya dauki matakin dakatar da tafiya ne, biyo bayan afkuwar gobarar.
Da sanyin safiyar Juma’a wani faifan bidiyo ya bazu a kafafen sada zumunta na zamani wanda ke nuna wadanda suka tsere daga lamarin suna ba da labarin abubuwan da suka faru a kan lamarin.