Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta kasa NRC, ta ce, za a ci gaba da aikin jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna ranar Talata.
An dakatar da zirga-zirgar layin dogo ne a ranar Juma’a bayan da jirgin kasa ya kauce hanya a tashar Kubwa da ke Abuja.
Hukumar ta sanar da ci gaba da aikin ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan ayyuka, Niyi Alli.
Sabanin jadawalin tafiye-tafiyen da aka yi na farko inda jiragen kasa guda biyu ke tashi daga Abuja da Kaduna a kullum, kamfanin ya daidaita yawan tafiye-tafiye na ranar Laraba zuwa daya daga kowane gefe.